HASBUNALLAHU WA,NI,IMAL WAKIL

Abin takaici an kama wannan matar mai suna Aisha Abubakar ta ษ—auko harsashin bindiga sama da guda dubu biyu daga Abuja zata kaiwa ษ“arayin daji, ฦดan ta'adda masu garkuwa da mutane a garin ฦณantumaki ฦ™aramar hukumar ฦŠan-Musa a nan jihar Katsina

Wallahi ana cutar damu abun ban haushi da takaici, wai yanzu ace da mutanenmu za'a dinga haษ—a kai domin wargaza zaman lafiyarmu?, kuma mutanen mata ba maza ba, mata da aka sansu da tsananin tausayi da jin kai, domin zaku ga yanzu matane akafi kamawa suna kaiwa baryin daji makamai

Tabbas Hakan ya ฦ™ara tabbatar wa, duk taddancin da ษ“arayin daji ke yi akwai gurษ“atattun mutane a cikinmu da suke taimaka musu don kawai su samu kuษ—i, don haka matsalar yaฦ™i da ฦดan bindiga ba wai laifin Gwamnati bane kaษ—ai, yanzu wannan da ace ta samu nasaran isar da alburusan ga ฦดan bindiga Allah kaษ—ai Ya san ษ“arnan da za'ayi da su, don haka jama'a a cigaba da bawa jami'an tsaro haษ—in kai da bayanan sirri

Kamar yadda zakuji matar ta faษ—a da bakinta, tace wai yunwa ne ya sakata aikata wannan mummunan aiki, kuma wai shine karo na farko, akwai cikakken bidiyo na tambayoyin da aka mata tana amsawa a Comment Section nawa ๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡

Amma ni ba zan taษ“a yadda da uzurin yunwa ba, ace mutum saboda yunwa zai je ya aikata laifi mai muni irin wannan, wanda za'a kashe ฦดan uwansa da shi

Allah Ya sauwaฦ™e, Ya kawo mana ฦ™arshen wannan masifa Ameen ya hayyu ya quyyum ๐Ÿ™๐Ÿ™๐Ÿ™๐Ÿ™



Ya Allah kakaratsare AL'FARMAR ANNABI MUHAMMAD S A W.๐Ÿคฒ๐Ÿคฒ๐Ÿคฒ


Post a Comment

Previous Post Next Post

Contact Form