Abin takaici an kama wannan matar mai suna Aisha Abubakar ta ษauko harsashin bindiga sama da guda dubu biyu daga Abuja zata kaiwa ษarayin daji, ฦดan ta'adda masu garkuwa da mutane a garin ฦณantumaki ฦaramar hukumar ฦan-Musa a nan jihar Katsina
Wallahi ana cutar damu abun ban haushi da takaici, wai yanzu ace da mutanenmu za'a dinga haษa kai domin wargaza zaman lafiyarmu?, kuma mutanen mata ba maza ba, mata da aka sansu da tsananin tausayi da jin kai, domin zaku ga yanzu matane akafi kamawa suna kaiwa baryin daji makamai
Tabbas Hakan ya ฦara tabbatar wa, duk taddancin da ษarayin daji ke yi akwai gurษatattun mutane a cikinmu da suke taimaka musu don kawai su samu kuษi, don haka matsalar yaฦi da ฦดan bindiga ba wai laifin Gwamnati bane kaษai, yanzu wannan da ace ta samu nasaran isar da alburusan ga ฦดan bindiga Allah kaษai Ya san ษarnan da za'ayi da su, don haka jama'a a cigaba da bawa jami'an tsaro haษin kai da bayanan sirri
Kamar yadda zakuji matar ta faษa da bakinta, tace wai yunwa ne ya sakata aikata wannan mummunan aiki, kuma wai shine karo na farko, akwai cikakken bidiyo na tambayoyin da aka mata tana amsawa a Comment Section nawa ๐๐๐๐๐๐๐๐๐๐๐๐๐๐๐๐
Amma ni ba zan taษa yadda da uzurin yunwa ba, ace mutum saboda yunwa zai je ya aikata laifi mai muni irin wannan, wanda za'a kashe ฦดan uwansa da shi
Allah Ya sauwaฦe, Ya kawo mana ฦarshen wannan masifa Ameen ya hayyu ya quyyum ๐๐๐๐
Ya Allah kakaratsare AL'FARMAR ANNABI MUHAMMAD S A W.๐คฒ๐คฒ๐คฒ


