SARKIN MALAMAI MEDIA TEAM KATSINA STATE

 SARKIN MALAMAI MEDIA TEAM KATSINA STATE






Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru RaΙ—Ι—a PhD CON ya amshi tawaga mai Ζ™arfi daga Hukumar UNDP a Filin Jirgin Ƙasa da Ƙasa na tunawa da Marigayi Malam Umaru Musa Ζ³ar'adua dake Katsina.

Tawagar UNDP tazo Katsina ne domin halartar Babban Taron Masu Ruwa da Tsaki na Shiyyar Arewa maso Yamma domin tattaunawa akan matsalar Tsaron data addabi yankin.

Hakanan kuma tawagar UNDP ta samu jagorancin Babban Wakilin Hukumar ta Ƙasa Nigeria, Mr. Attafuah.

Wannan ya nuna jajir cewar Gwamna RaΙ—Ι—a akan magance matsalolin tsaron dake addabar Jihar Katsina, Yankin Arewa maso Yamma dama Ƙasa baki Ι—aya.

Rabiatu Sulaiman Kurfi 
S.A Digital Media to 
Katsina State Governor

Shared by Pharm Yarima Angawa Chairman for Sarkin Malamai Media Team Katsina State..

Post a Comment

Previous Post Next Post

Contact Form